A ranar Talata, 21 ga Yuli, gwamnatin ƙasar Bangladesh ta sanar da kunshin rabe-raben kuɗin aikin Hajjin shekarar 2027 guda uku, inda biyu daga cikinsu daga gwamnatin ƙasar ne, yayin da ɗaya zai kasance na alhazan da za su tafi ta hannun kamfanonin jigilar aikin Hajji masu zaman kansu, bayan rage kuɗin tikitin jirgi zuwa Taka130,000.
Ministan Harkokin Addini, Kazi Shah Mofazzal Hossain Kaikobad, ya ce za a baiwa kamfanonin jigilar aikin Hajji masu zaman kansu damar ƙara wasu tsarin kuɗin aikin Hajji guda uku baya ga daidaitaccen tsarin da gwamnati ta amince da shi.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai da aka gudanar a ɗakin taro na Ma’aikatar Harkokin Addini da ke Sakatariyar Gwamnatin Bangladesh a ranar 21 ga Yuli.
Ya ce kwamitin zartarwa mai kula da harkokin Hajji ne ya amince da waɗannan tsare-tsare.
A ƙarƙashin tsarin gwamnati, kuɗin Kunshin Hajji na 1 zai kai Ta dubu 615,263, yayin da Kunshin kuɗin Hajji na 2, wanda aka bayyana a matsayin mafi sauƙin farashi, zai kai TK 505,648.















