Kotun majistare mai lamba 4, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Mustapha Sa’ad Datti ta aike da wani mutum mai suna Saleh Yakubu zuwa gidan yari bisa zargin sa da harƙallar filaye da gidaje d jihar Kano.
Freedom Radio ta rawaito cewa an gurfanar da Yakubu ne a ranar Alhamis, inda a takardar tuhumar yansanda, ake cajin sa da laifin yin sojan-gona da ɓata suna.
Bayan karanto masa laifukan da ake tuhumar sa da su, Yakubu ya musanta
Daga nan ne sai mai gabatar da ƙara ta roƙi kotu da ta sanya wata ranar domin su kawo shaidu, inda kotun ta amince, ta kuma sanya ranar 7 ga watan Satumba, 2026 domin sake gabatar da wanda ake zargin, ta kuma bada umarnin a kai shi gidan gyaran hali a ajiye zuwa ranar.
Tun da fari, ana zargin Yakubu da amfani da stamfi (stamp), mallakin Dagacin unguwar Dausayi, Abdu Muhammad Dausayi, wajen yin harƙallar filaye da gidaje.
Ana tuhumar Yakubu da buga wannan stamfi akan takardun filaye da gidaje na bogi da sunan Dagacin.
















