Kamfanin hayar mota na duniya, Uber, ya sanar da shirin rufe ayyukansa a ƙasashen Najeriya da Uganda, wanda zai fara aiki daga yau Laraba, 2 ga watan Satumba, 2026.
A cikin wata sanarwa da kamfanin ya aikewa Nairametrics, Uber ya ce matakin ya biyo bayan “nazari mai zurfi” da ya gudanar, kuma ya ga cewa ba wata riba da ya ke samu a Najeriya da Uganda kamar yadda ya ke a sauran ƙasashen Afirka.
Uber ya ce: “Bayan gudanar da nazari mai zurfi, mun ɗauki mataki mai tsauri na rufe ayyukanmu a Najeriya da Uganda, daga ranar 2 ga Satumba, 2026.”
Kamfanin ya bayyana cewa babban abin da ya fi mayar da hankali a kai a yanzu shi ne tallafa wa direbobi, fasinjoji da ma’aikatan da ke aiki a ƙasashen biyu yayin da ake gudanar da wannan sauyi.
Nairametrocs ta rawaito cewa wannan mataki ya zo ne daidai lokacin da ma’aikata dubu 3,300 a ƙasashen biyu za su rasa aiki.















