Wani gini ya rushe a yankin Wuse Zone 4 da ke Abuja, sa’o’i kaɗan bayan Sashen Kula da Ci gaban Birane na Hukumar Babban Birnin Tarayya (FCTA) ya rufe ginin tare da umartar mazauna lciki da su fice daga wurin.
Jaridar VANGUARD ta rawaito cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 8:00 na dare ranar Litinin, inda ya haifar da aikin ceto da jami’an Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya da sauran jami’an agajin gaggawa ke gudanarwa, domin gano ko akwai mutanen da suka makale a ƙarƙashin baraguzan ginin.
An jibge motocin ɗaukar marasa lafiya guda uku a wurin, yayin da jami’an agajin gaggawa ke ci gaba da ƙoƙarin fitar da duk wani mutum da ka iya kasancewa cikin baraguzan ginin cikin gaggawa.
ADVERTISEMENT















