Majalisar Masarautar Kano ta ƙaryata wani faifan bidiyo da ya yaɗu a kafafen sada zumunta, wanda ke ikirarin cewa Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya faɗi a jarrabawa a wani kwas guda ɗaya, wato ya samu ‘carry-over’ a karatun fannin shari’ah da ya ke yi a Jami’ar Northwest da ke Kano.
Faifan bidiyon, wanda ya yadu sosai a kafafen sada zumunta a jiya Lahadi, ya yi ikirarin cewa Sarkin ya faɗi a jarrabawar ɗaya daga cikib kwasa-kwasan da ya ɗauka ba.
A halin yanzu, Sanusi yana karatun digiri na farko na Bachelor of Laws (LL.B), aji na biyu, a fannin Common Law da Shari’a a jami’ar.
Sai dai Muhammad Ado, Sakataren Ofishin Sarkin, ya ce wannan labari ba gaskiya ba ne, shifcin gizo ne kawai, yana mai tabbatar da cewa Sarkin yana kan hanyar kammala karatunsa da sakamako mafi girma wato first class.
A cewarsa, bayanan da Masarautar ta samu shije cewa Sarkin yana bukatar maki guda ne kawai domin samun sakamakon first class din.
Shi ma wani dalibin jami’ar, Ibrahim Abubakar-Danmasani, ya ƙaryata labarin, inda ya ce har zuwa ranar Lahadi, ba a fara ma jarrabawar dalibai a jami’ar ba ballantana ma har a ce Sarkin ya faɗi a jarrabawa.
Ya ce ana sa ran fara jarrabawar ne a ranar Litinin.
Itama Jami’ar ta tabbatar da cewa labarin ba gaslkya bane.















